Rundunar Sojojin Saman Kasar nan. ta sanar da cewa ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga, Mustapha Abdullahi, da wasu yaransa guda biyar a Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Arewa na Jihar Kaduna.
Daraktan watsa labarai da hulɗa da jama’a na rundurar, Edward Gabkwet ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce ɓangaren sojojin rundunar na musamman na 413 ne suka yi aikin.
Mista Gabkwet ya ce an tura sojojin ne bayan samun bayanan sirri a ranar 31 ga Agustan cewa ɗan bindigar tare da yaransa sun tunkari dajin Sabon Gida da ke kan hanyar Sabon Birni, inda ake tunanin sun nufa da zimmar garkuwa da mutane, ko cutarwar da wasu ko kashewa.
A cewarsa, ganin sojojin ke da wuya, sai ƴan bindigar suka buɗe wuta, wanda hakan ya sa sojojin suka mayar da martani har suka ci ƙarfinsu.
Sojojin sun samu nasarar kashe jagoran ƴan bindigar da yaransa, inda aka ƙwato bindigogin ƙirar gida da alburusai da wayoyoyi da layukan waya da sauransu.
“Muna cigaba da ƙoƙarin ganin mun fatattaki ƴan bindiga daga yankin Igabi da Birnin Gwari baki ɗaya.
“An kuma yaba wa ƙoƙarin sojojin tare da kira a gare su da ƙara ƙaimi a wannan aiki da suke yi na kare rayuwa da dukiyar al.umma,” inji shi.