fidelitybank

Siyasa: Tinubu ne fatan mu a 2022 – Gamayyar Kungiyoyin Dalibai

Date:

Gamayyar Kungiyoyin Cigaban Matasa da Shugabannin Dalibai (CPYS) ta ce za ta marawa Asiwaju Bola Tinubu baya a matsayin dan takarar shugaban kasa a 2023 idan har ya goyi bayan fitowar sa.

Shugaban gamayyar kungiyoyin, Samuel Olalere, ya sanar da hakan a wani taron manema labarai a ranar Lahadi a Ikeja, Legas.

Ya ce kungiyar ta amince da kasancewar Tinubu da gogewa a matsayin wanda ya yi fice a cikin manyan da su ka cancanta a cikin masu neman kujerar shugaban kasa.

Ya ce,“Shugabanci, musamman a matakin shugaban kasa, galibi ba aikin fada da karfin jiki ba ne.

“Wannan shi ne dalilin da ya sa mu ka yi imanin cewa shugaban Najeriya a 2023 ya kamata ya kasance mutum ne da ya dace da shekarun da su ka dace, wanda ya tabbatar da cewa zai iya ganowa da kuma tura dimbin hazaka ga Najeriya domin ciyar da kasar gaba.”

“Mutumin da ya dace da wannan kudiri a hasashenmu shi ne Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, jagoran jam’iyyar APC na kasa,” inji Olalere.

A cewarsa, Tinubu ya mallaki hadakar kwarewa da kuma hanyar sadarwa da za ta bai wa Najeriya irin shugabancin da ya dace.

A jawabin sa ya ce“Ba zan yi watsi da muryoyin da ke kirana da in tsaya takarar shugabancin kasa a 2023 ba”. Inji Tinubu.

Sai dai ya ce dole ne Tinubu da jam’iyyar APC su daidaita tsakanin jagoran gwamnati da shugaban jam’iyyar ta hanyar baiwa matasa mukamin shugaban kasa.

Olalere ya ce dole ne jam’iyyar ta biya bukatun matasa a cikin shirye-shiryen siyasa na 2023 masu tasowa, domin samun daidaito na tsararraki a cikin daidaiton iko.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp