Gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike, ya ce, jam’iyyarsa ta PDP, za ta karbe kujerar shugaban kasa da a ke nema ruwa a jallo daga jam’iyya mai mulki ta APC a shekarar 2023 idan hukumar zabe mai zaman kanta ta ci gaba da tsarinta na gudanar da zabe ba tare da katsalandan ba.
Wike ya bayyana haka ne a ranar Litinin a wajen kaddamar da wasu ayyuka a jihar Rivers a lokacin bikin cikarsa shekaru 58 da haihuwa.
A halin yanzu dai jam’iyyar PDP ce ke rike da jihohi 13, yayin da jam’iyyar APGA ke da daya inda jam’iyyar APC ta mamaye sauran.
A ‘yan kwanakin nan ‘yan siyasan adawa da kungiyoyin farar hula sun yaba wa INEC kan bullo da tsare-tsare da ake amfani da su wajen tantancewa a lokacin zabe.
Da ya ke magana a ranar Litinin, Wike ya yabawa INEC a karkashin shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, kan tsayawar da ta yi na nuna adawa da magudin zabe da kuma tsoratar da siyasa.
Gwamnan Ribas ya ce, “Da yardar Allah PDP za ta karbi mulki a 2023. Ina addu’ar INEC ta ci gaba da tsarin da ta bullo da shi, inda kowa zai je ya yi yakin neman zabe, kuri’ar mutane za ta kirga, domin idan kuri’un mutane za su kirgu. Yanzu masu rike da mukaman siyasa za su yi lissafi. Lokacin da kuri’un ku ba su kirga ba, masu rike da mukaman siyasa ba za su yi wa mutane hisabi ba”. Inji Wike.