fidelitybank

Siyasa: PDP ce za ta lashe zaben 2023 – Nyesom Wike

Date:

Gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike, ya ce, jam’iyyarsa ta PDP, za ta karbe kujerar shugaban kasa da a ke nema ruwa a jallo daga jam’iyya mai mulki ta APC a shekarar 2023 idan hukumar zabe mai zaman kanta ta ci gaba da tsarinta na gudanar da zabe ba tare da katsalandan ba.

Wike ya bayyana haka ne a ranar Litinin a wajen kaddamar da wasu ayyuka a jihar Rivers a lokacin bikin cikarsa shekaru 58 da haihuwa.

A halin yanzu dai jam’iyyar PDP ce ke rike da jihohi 13, yayin da jam’iyyar APGA ke da daya inda jam’iyyar APC ta mamaye sauran.

A ‘yan kwanakin nan ‘yan siyasan adawa da kungiyoyin farar hula sun yaba wa INEC kan bullo da tsare-tsare da ake amfani da su wajen tantancewa a lokacin zabe.

Da ya ke magana a ranar Litinin, Wike ya yabawa INEC a karkashin shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, kan tsayawar da ta yi na nuna adawa da magudin zabe da kuma tsoratar da siyasa.

Gwamnan Ribas ya ce, “Da yardar Allah PDP za ta karbi mulki a 2023. Ina addu’ar INEC ta ci gaba da tsarin da ta bullo da shi, inda kowa zai je ya yi yakin neman zabe, kuri’ar mutane za ta kirga, domin idan kuri’un mutane za su kirgu. Yanzu masu rike da mukaman siyasa za su yi lissafi. Lokacin da kuri’un ku ba su kirga ba, masu rike da mukaman siyasa ba za su yi wa mutane hisabi ba”. Inji Wike.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp