Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Dr. Iyorchia Ayu ya yi hasashen dawowar ministan ayyuka na musamman da harkokin gwamnati, Sanata George Akume zuwa PDP.
Ya ce nan ba da jimawa ba ministan wanda shi ne shugaban jamâiyyar APC a yankin Arewa ta tsakiya zai dawo PDP.
Ayu ya bayyana hakan ne a garin Gboko a lokacin da a ke shirin ficewar dan majalisar wakilai, John Dyeh daga APC zuwa PDP.
âAkume zai dawo PDP. Ina faÉin wannan magana bisa ga abin da na saniâ. inji Ayu.
âA baya na annabci cewa Akume zai rike tsintsiya kuma ya yi. Yanzu ina annabata cewa zai dawo PDP. Idan ya dawo kar ka ki shi, amma ka tabbatar ka gyara shi, domin a inda ya ke a yanzu ba a tsaye ya ke tunani ba. Ya kasance ya rasa Éan sa nahikaa. Sai dai a gyara masa sannan a tabbatar ya yi tunani da kyau,â inji Ayu.
Ayu wanda ya karbi bakoncin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gboko/Tarka a majalisar wakilai ya ce, shi (Dyeh) ya ga hasken kuma ya yi alkawarin cewa za a yi wa duk wadanda suka sauya sheka adalci.
Gwamnan jihar, Samuel Ortom ya yi maraba da dan majalisar tarayya da sauran wadanda suka sauya sheka.
Shugaban masu sauya shekar, Dyeh, ya ce ya yanke shawarar ficewa daga PDP zuwa APC ne saboda shugaban kasa kawunsa ne.