Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta gurfanar da mutanan da ta kama wand ake zargi da yunkurin kona ofishin dan takarar gwamana jihar Kano, Sanata Barau Jibril.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai.
Ya ce”Mu na tuhumar matasan su 13 da laifin hada baki da tayar da tarzoma da yin sata da ta’ammali da miyagun kwayoyi da kuma yin taro ba bisa ka’idab da muggan makamai wanda hakan ya sa muka gurfanarda matasan a Kotu, a binciken da muka gudanar mun gano cewa akwai wasu mutane da suke da hannu akan aikata laifin da ake tuhumar matasan da aikatawa, kuma yanzu haka mun baza komarmu domin kamo su.” Inji DSP Kiyawa.