fidelitybank

Siyasa: Buhari da kansa ya taya ni murna – Zago

Date:

Shugaban tsagin bangaren jam’iyyar APC a jihar Kano, Ahmadu Haruna Zago, ya gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Ahmadu Zago, wanda bangaren tsohon gwamnan jihar, Sanata Ibrahim Shekarau ya zaba a matsayin shugaban jam’iyyar, ya gana da shugaban kasar ne a yayin da a ke ci gaba da rikici kan shugabancin APC reshen jihar ta Kano tsakaninsa da Abdullahi Abbas na bangaren Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.

Rikicin ya samo asali ne bayan Sanata Shekarau da wasu ‘yan majalisar dokokin tarayya sun balle daga bangaren Gwamna Ganduje inda suka zarge shi da rashin iya shugabanci.

Hakan ya sa bangarorin biyu kowanne ya gudanar da zabukan shugabannin jam’iyyar ta APC a watan Okotoban da ya gabata.

Rikicin ya kai su gaban kuliya kuma a hukuncin da wata kotun tarayya da ke Abuja babban birnin kasar ta yanke ta ce Ahmadu Zago ne halastaccen shugaban jam’iyyar ta APC.

Sai dai jam’iyar ta APC bangaren gwamnatin jihar Kano ta ce har yanzu ba ta karaya ba kuma za ta bi dukkan hanyoyin da suka dace wajen ganin ta kwace shugabancin jam’iyyar.

A tattaunawarsa da BBC Hausa bayan ganawa da shugaban kasa, Ahmadu Zago, ya ce”Shugaba Buhari ya taya ni murnar yin nasarar samun shugabancin APC a jihar ta Kano”.

“Shi shugaban kasa ya tambaye ni ‘me a ka samu?’, ni kuma na ce masa ‘an samu shugabancin APC a Kano. Daga nan ne ya taya ni murna”, a cewar Ahmadu Zago.

Amma ya kara da cewa ba su tattauna kan rikicin da jam’iyyar ta ke fama da shi a jihar Kano ba, ya na mai cewa “Tun da batun ya na kotu ba mu tattauna a kansa ba. Ka san shugaban kasa ba ya shiga lamarin da ke gaban kotu.”

Da BBC su ka tambaye shi kan jita-jitar da ke cewa akwai yiwuwar su hade da tsohon gwamnan jihar ta Kano, Rabi’u Kwankwaso, Ahmadu Zago ya ce “babu wannan batu. Sai dai ka san ita siyasa babu masoyi ko makiyi na dindindin.”

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp