Shugaban tsagin bangaren jam’iyyar APC a jihar Kano, Ahmadu Haruna Zago, ya gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Ahmadu Zago, wanda bangaren tsohon gwamnan jihar, Sanata Ibrahim Shekarau ya zaba a matsayin shugaban jam’iyyar, ya gana da shugaban kasar ne a yayin da a ke ci gaba da rikici kan shugabancin APC reshen jihar ta Kano tsakaninsa da Abdullahi Abbas na bangaren Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.
Rikicin ya samo asali ne bayan Sanata Shekarau da wasu ‘yan majalisar dokokin tarayya sun balle daga bangaren Gwamna Ganduje inda suka zarge shi da rashin iya shugabanci.
Hakan ya sa bangarorin biyu kowanne ya gudanar da zabukan shugabannin jam’iyyar ta APC a watan Okotoban da ya gabata.
Rikicin ya kai su gaban kuliya kuma a hukuncin da wata kotun tarayya da ke Abuja babban birnin kasar ta yanke ta ce Ahmadu Zago ne halastaccen shugaban jam’iyyar ta APC.
Sai dai jam’iyar ta APC bangaren gwamnatin jihar Kano ta ce har yanzu ba ta karaya ba kuma za ta bi dukkan hanyoyin da suka dace wajen ganin ta kwace shugabancin jam’iyyar.
A tattaunawarsa da BBC Hausa bayan ganawa da shugaban kasa, Ahmadu Zago, ya ce”Shugaba Buhari ya taya ni murnar yin nasarar samun shugabancin APC a jihar ta Kano”.
“Shi shugaban kasa ya tambaye ni ‘me a ka samu?’, ni kuma na ce masa ‘an samu shugabancin APC a Kano. Daga nan ne ya taya ni murna”, a cewar Ahmadu Zago.
Amma ya kara da cewa ba su tattauna kan rikicin da jam’iyyar ta ke fama da shi a jihar Kano ba, ya na mai cewa “Tun da batun ya na kotu ba mu tattauna a kansa ba. Ka san shugaban kasa ba ya shiga lamarin da ke gaban kotu.”
Da BBC su ka tambaye shi kan jita-jitar da ke cewa akwai yiwuwar su hade da tsohon gwamnan jihar ta Kano, Rabi’u Kwankwaso, Ahmadu Zago ya ce “babu wannan batu. Sai dai ka san ita siyasa babu masoyi ko makiyi na dindindin.”