fidelitybank

Rundunar Soji ta saki sojan da ta amince da yin aure

Date:

Rundunar Sojin Najeriya ta saki wata Soja mai suna Sofiat Akinlabi da a ka tsare bayan wani namijin kokarin da ta yi a sansanin horar da matasa masu yi wa kasa hidima a jihar Kwara.

Kakakin rundunar sojin Najeriya, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ne ya tabbatar da hakan a ranar Asabar.

Ya ce, “Zan iya tabbatar muku da cewa an ba da umarnin a saki sojan, kuma ya ji dadin bikin Kirsimeti tare da ‘yan uwa da abokan arziki tare da yi mata gargadi mai tsanani da kada ta sake yin irin wannan abu.”

Idan dai za a iya tunawa, rundunar sojin ta yi ikirarin cewa an tsare sojan ne, saboda ya saba wa dokokin soji da su ka haramta nuna soyayya ga jama’a da wani ma’aikacin jami’an tsaro.

Mai magana da yawun rundunar sojin wanda ya tabbatar da kamen makonnin da suk a gabata ya kara da cewa sojan ta saba ka’idojin rundunar sojin Najeriya kan yadda jami’an sojin ke gudanar da ayyukansu a lokacin da a ka tura su bakin aiki.

Nwachukwu ya ce ba a sa ran sojan macen za ta kasance da wata alaka mai ban sha’awa da wanda a ke horarwa; shiga cikin soyayya yayin da su ke sanye da kayan sawa, sannan kuma ya na da laifin kin bin umarnin rundunar soji na tsaye da kuma umarnin amfani da kafafen sada zumunta.

Tun a baya ne dai a ka ta matsa lamba a kan a saki soja mace wadda ta sumbaci masoyin ta a lokacin da ya amince zai aure ta a sansanin masu yi wa kasa hidima.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp