Kasar Sin za ta dauki tsattsauran matakai, idan har Taiwan ta yi yunkurin samun ‘yancin kai.
Wani jami’in kasar Sin ne ya sanar da hakan a ranar Laraba, ya kara da cewa tsokanar Taiwan da tsoma baki a waje na iya kara tsanantawa a shekara mai zuwa.
Kasar Sin ta yi ikirarin cewa yankin Taiwan mai mulkin dimokuradiyya ne, kuma a cikin shekaru biyu da suka gabata, ta kara matsa kaimi a fannin soji da na diflomasiyya, domin tabbatar da ikonta, lamarin da ya kara fusata birnin Taipei da kuma nuna damuwa a birnin Washington.
Kakakin ofishin kula da harkokin Taiwan Ma Xiaoguang ya shaidawa manema labarai a taron cewa, kasar Sin ta na son yin iyakacin kokarinta na neman sake hadewa da kasar Taiwan cikin lumana, amma za ta dauki mataki idan a ka keta layukan da ta shata mata a kan samun’yancin kai.
Ya kuma ce Idan sojojin ‘yan aware a Taiwan masu neman ‘yancin kai suka tunzura, ko su yi amfani da karfi ko ma su bi ta kowace hanya, to dole ne su dauki tsauraran matakai.