Kungiyar Kare Hakkokin Tattalin Arziki ta Kasa ta mayar da martani game da janye lasisin makarantu masu zaman kansu da Gwamna Abdullahi Ganduje ya yi a jihar Kano.
A ranar Litinin ne gwamnatin jihar Kano ta kwace lasisin gudanar da dukkan makarantu masu zaman kansu a jihar.
Gwamna Ganduje ya dauki matakin ne biyo bayan kisan wata yarinya ‘yar shekara biyar mai suna Hanifa Abubukar da Abdulmalik Tanko, mallakin makarantar Noble Kids Academy da ke karamar hukumar Nasarawa ta jihar ya kashe ta.
Kwamishinan Ilimi na jihar, Sunusi Sa’id Kiru, yayin da yake magana a ranar Litinin ya ce, za a sake duba lasisin da aka soke tare da sabunta su bayan an tantance su.
A martaninta, SERAP ta yi Allah-wadai da matakin, inda ta roki Ganduje da ya janye matakin, saboda hakan na iya kara ta’azzara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.
Kungiyar farar hula ta ce jihar Kano ce ta fi kowacce yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yanzu da 989,234.
SERAP ta bayyana hakan ne a shafin Twitter a yammacin ranar Talata.
Ta ce, “Muna kira ga gwamnan jihar Kano @GovUmarGanduje da ya gaggauta janye dakatarwar da aka yi wa duk wasu makarantu masu zaman kansu na jihar ba bisa ka’ida ba.
“Kano ce ta fi kowacce yawan yaran da ba su zuwa makaranta (989,234).