fidelitybank

SERAP ta mayar da martani a kan janye lasisin makarantun Kano

Date:

Kungiyar Kare Hakkokin Tattalin Arziki ta Kasa ta mayar da martani game da janye lasisin makarantu masu zaman kansu da Gwamna Abdullahi Ganduje ya yi a jihar Kano.

A ranar Litinin ne gwamnatin jihar Kano ta kwace lasisin gudanar da dukkan makarantu masu zaman kansu a jihar.

Gwamna Ganduje ya dauki matakin ne biyo bayan kisan wata yarinya ‘yar shekara biyar mai suna Hanifa Abubukar da Abdulmalik Tanko, mallakin makarantar Noble Kids Academy da ke karamar hukumar Nasarawa ta jihar ya kashe ta.

Kwamishinan Ilimi na jihar, Sunusi Sa’id Kiru, yayin da yake magana a ranar Litinin ya ce, za a sake duba lasisin da aka soke tare da sabunta su bayan an tantance su.

A martaninta, SERAP ta yi Allah-wadai da matakin, inda ta roki Ganduje da ya janye matakin, saboda hakan na iya kara ta’azzara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Kungiyar farar hula ta ce jihar Kano ce ta fi kowacce yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yanzu da 989,234.

SERAP ta bayyana hakan ne a shafin Twitter a yammacin ranar Talata.

Ta ce, “Muna kira ga gwamnan jihar Kano @GovUmarGanduje da ya gaggauta janye dakatarwar da aka yi wa duk wasu makarantu masu zaman kansu na jihar ba bisa ka’ida ba.

“Kano ce ta fi kowacce yawan yaran da ba su zuwa makaranta (989,234).

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan ÆŠaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp