fidelitybank

SERAP ta mayar da martani a kan janye lasisin makarantun Kano

Date:

Kungiyar Kare Hakkokin Tattalin Arziki ta Kasa ta mayar da martani game da janye lasisin makarantu masu zaman kansu da Gwamna Abdullahi Ganduje ya yi a jihar Kano.

A ranar Litinin ne gwamnatin jihar Kano ta kwace lasisin gudanar da dukkan makarantu masu zaman kansu a jihar.

Gwamna Ganduje ya dauki matakin ne biyo bayan kisan wata yarinya ‘yar shekara biyar mai suna Hanifa Abubukar da Abdulmalik Tanko, mallakin makarantar Noble Kids Academy da ke karamar hukumar Nasarawa ta jihar ya kashe ta.

Kwamishinan Ilimi na jihar, Sunusi Sa’id Kiru, yayin da yake magana a ranar Litinin ya ce, za a sake duba lasisin da aka soke tare da sabunta su bayan an tantance su.

A martaninta, SERAP ta yi Allah-wadai da matakin, inda ta roki Ganduje da ya janye matakin, saboda hakan na iya kara ta’azzara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Kungiyar farar hula ta ce jihar Kano ce ta fi kowacce yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yanzu da 989,234.

SERAP ta bayyana hakan ne a shafin Twitter a yammacin ranar Talata.

Ta ce, “Muna kira ga gwamnan jihar Kano @GovUmarGanduje da ya gaggauta janye dakatarwar da aka yi wa duk wasu makarantu masu zaman kansu na jihar ba bisa ka’ida ba.

“Kano ce ta fi kowacce yawan yaran da ba su zuwa makaranta (989,234).

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da ÆŠumi-ÆŠumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya É“ata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buÉ—e shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp