Kasar Senegal ta kai wasan daf da na kusa da na karshe, bayan ta doke Cape Verde 2-0 a wasan zagayen 16 a gasar Kofin Ƙasashen Afirka da ke gudana a Kamaru.
Tauraron ɗan wasa Sadio Mane ne ya fara zira ƙwallo a ragar Cape Verde jim kaɗan bayan an bai wa mai tsaron raga Vozinha jan kati, sakamakon karon da suka yi da ɗan wasan na Liverpool.
Mane ya ci gaba da wasan duk da kaɗuwar da ya yi bayan karon, sai dai bai ci gaba da wasan ba, inda Ahmadou Bamba Dieng ya karɓe shi a minti na 70.
Ana cikin ƙarin lokaci ne kuma Dieng ya ƙara ta biyu.
Senegal za ta kara da ƙungiyar da ta yi nasara a wasan Malawi da Morocco, wanda ke gudana yanzu haka, har ma Malawi ta ci 1-0.