Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano ta kori dalibai 83, yayin da ta gargadi 25, sannan ta gargadi 10 daga cikin su.
Hukumar Kwalejin Kimiyya da Fasaha, reshen jihar Kano ta bayyana hakan ne a taronta na 90 da ta gudanar a ranar Litinin 29 ga watan Nuwamba, 2021, ta yi nazari kan rahotannin da ta samu na cin hanci da rashawa da kuma sakamakon bogi, domin haka ta amince da hukuncin.
Solacebase ta rawaito cewa hukumar ta amince da hukuncin a taronta na 90 da ta gudanar bayan duba rahotannin rashin da’ar jarabawa da sakamakon bogi.
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na cibiyar, Auwal Isma’il Bagwai ya fitar a ranar Laraba, ta ce mataimakin magatakardar makarantar, Mal. Garba Isma’il Fagge ya bayyana hakan ne jim kadan bayan kammala taron, inda ya bayyana cewa hukumar ba ta za lamibnci hakan ba.