Ministan ilimi, Adamu Adamu, ya buƙaci hukumomin shirya jarrabawa a Najeriya da su yi amfani da fasahar zamani wajen magance matsalar satar amsa lokacin jarrabawa.
Ministan ya bayyana haka ne a lokacin buɗe taron tattaunawa kan yadda za a magance satar amsa, wanda majalisar dokokin Najeriya da hukumar shirya jarrabawa ta ƙasa (NECO) suka shirya a Legas.
Adamu ya ce “satar amsa lokacin jarrabawa babbar matsala ce da ke illa ga yadda hukumomi ke shirya jarrabawa a Najeriya.”
Ya ce Najeriya ƙasa ce da take baya a harkar magance satar amsa.
Ya ƙara da cewa ya zama wajibi a yi amfani da fasahar zamani wajen ganin an tsaftace harkar jarrabawa ta ƙasar.