fidelitybank

Sarkin Daura ya naɗa Yusuf Buhari a matsayin Talban Daura, shekaru 2 bayan ya baiwa Alpha Conde sarautar

Date:

Sarkin Daura, Umar Faruk Umar ya naɗa Yusuf Buhari, ɗan gidan Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a matsayin Talban Daura.
A watan Agusta na shekarar 2019, Sarkin Daura ya naɗa Shugaban Kasar Gini na wannan lokacin, Alpha Conde a matsayin Talban Daura.
Bayan ya naɗawa Conde rawanin Talban Daura, Sarkin ya kuma kyautar doki, takobi da shanu, inda ya ce ya cancanci tagomashin sakamakon kaunar da ya ke yinwa Buhari.
Duk da cewa har yanzu Shugaban Kasar Gini ɗin ne mai riƙe da sarautar, a watan Satumbar nan kuma sai Sarkin ya sanar da cewa ya naɗa Yusuf Buhari a matsayin Talban Daura.
A jiya Asabar ne a ka yi gagarumin bikin naɗin sarautar a fadar Sarkin Daura.
A wajen bikin, Sarkin ya baiyana cewa an naɗa Yusuf Buhari a matsayin Talban Daura kuma Hakimin Kwasarawa sakamakon irin ci gaban da mahaifinsa ya kawowa garin Daura.
Ya yi bayanin cewa ɗan gidan Shugaban Kasar zai rika zuwa masarautar Daura a -kai -a- kai domin bada gudunmawar sa a wajen ci gaban garin.
Waɗanda su ka halarci bikin sun haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Yemi Osibanjo, Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmed Lawan da Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila.
Sauran sun haɗa da Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje da takwaransa na Katsina, Aminu Masari da sauran manyan baƙi.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘ƴan ƙungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...
X whatsapp