fidelitybank

Sarkin Ban Kano: Mukhar Adnan ya rasu ya na da shekaru 95

Date:

Sarkin Ban Kano kuma hakimin Dambatta, Mukhtar Adnan ya rasu, sakamakon gajeriyar rashin lafiya da ya yi a ranar Juma’a.

Wata majiya mai tushe ta tabbatar da rasuwar mariyai Mukhtar Adnan mai shekaru 95, a safiyar ranar Juma’a, inda ta ce ya rasu kwanaki biyu bayan jinyarsa a wani asibiti mai zaman kansa, UMC Zhahir, a Kano.

Ya rasu ne da misalin karfe 4 na safiya, kwana biyu kacal bayan an sallame shi. Za a yi Jana’izarsa a yau bayan Sallar Juma’a a Dambatta.

Sarki Muhammadu Sunusi na Daya ne dai ya nada shi a matsayin Sarkin Bai a shekarar 1954 marigayi sarkin ya halarci zaben sarakunan Muhammadu Inuwa a watan Afrilu 1963, Ado Bayero a watan Oktoba 1963, Muhammadu Sanusi II a watan Yuni 2014 da kuma Aminu Bayero a watan Maris 2020.

An haifi Alhaji Mukhtar Adnan a shekarar 1926 kuma tsohon sarkin Kano Sir Muhammad Sanusi ne ya naɗa shi a matsayin sarkin Bai a shekarar 1954 domin ya gaji mahaifinsa Sabon Dambazau.

Marigayi Sarkin Bai shi ne kwamishinan ilimi na farko a jihar Kano a 1968, kuma ya halarci makarantar Elementary da ke Ɗambatta da makarantar Midil ta Kano da kuma makarantar malamai a garin Zaria.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp