fidelitybank

Sarkin Ban Kano: Mukhar Adnan ya rasu ya na da shekaru 95

Date:

Sarkin Ban Kano kuma hakimin Dambatta, Mukhtar Adnan ya rasu, sakamakon gajeriyar rashin lafiya da ya yi a ranar Juma’a.

Wata majiya mai tushe ta tabbatar da rasuwar mariyai Mukhtar Adnan mai shekaru 95, a safiyar ranar Juma’a, inda ta ce ya rasu kwanaki biyu bayan jinyarsa a wani asibiti mai zaman kansa, UMC Zhahir, a Kano.

Ya rasu ne da misalin karfe 4 na safiya, kwana biyu kacal bayan an sallame shi. Za a yi Jana’izarsa a yau bayan Sallar Juma’a a Dambatta.

Sarki Muhammadu Sunusi na Daya ne dai ya nada shi a matsayin Sarkin Bai a shekarar 1954 marigayi sarkin ya halarci zaben sarakunan Muhammadu Inuwa a watan Afrilu 1963, Ado Bayero a watan Oktoba 1963, Muhammadu Sanusi II a watan Yuni 2014 da kuma Aminu Bayero a watan Maris 2020.

An haifi Alhaji Mukhtar Adnan a shekarar 1926 kuma tsohon sarkin Kano Sir Muhammad Sanusi ne ya naɗa shi a matsayin sarkin Bai a shekarar 1954 domin ya gaji mahaifinsa Sabon Dambazau.

Marigayi Sarkin Bai shi ne kwamishinan ilimi na farko a jihar Kano a 1968, kuma ya halarci makarantar Elementary da ke Ɗambatta da makarantar Midil ta Kano da kuma makarantar malamai a garin Zaria.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...
X whatsapp