fidelitybank

Sally ya aza harhashin ginin tashar ruwa

Date:

Shugaban kasar Senegal, Macky Sall ya aza harsashin tubalin ginin tashar ruwa mai kimanin  dalar Amurka biliyan 1.13 da kamfanin DP World na kasar Dubai mallakar gwamnatin kasar hadadiyar daular larabawa da za ta gina a Ndayane mai tazarar kilomita 50 daga Kudu da Dakar babban birnin kasar.

Kamfanin DP World  na hadin gwiwa ne tsakanin kamfanin samar da kayayyaki da ke Dubai da kuma hukumar kula da tashar jiragen ruwa ta Dakar (PAD), shi ne babban jari mai zaman kansa a kasar da ke yammacin Afirka za ta samu.

Shugaba Mavky Salla ya ce, “Muna shirye domin sauya tsarin tattalin arzikinmu tare da wannan babban aikin,” in ji Sall.

Kamfanin DP World ya ce kashi na farko zai hada da na’urar ruwa mai tsawon mita 840 da tashar ruwa mai tsawon kilomita 5 da a ka kera domin sarrafa jiragen ruwa mai tsawon mita 366, yayin da kashi na biyu za a kara kwatankwacin mita 410 da kuma ci gaba da toshe tasoshin ruwa mai tsawon mita 400.

Shugaban DP World, Sultan Ahmed bin Sulayem, ya ce kamfaninsa zai bunkasa tare da sarrafa tashar sauke kwantena mai girman kadada 300, da kuma samar da kudade da kuma tsara ayyukan filaye da na ruwa.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp