fidelitybank

Sake Fasali: El-Rufa’I zai kashe Naira biliyan 1.4 a makarantu jihar

Date:

Gwamnatin jihar Kaduna ta ware Naira biliyan 1.4 domin sake fasalin gina makarantu da shirye-shiryen samar da kayan aiki a fadin jihar baki daya.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN ya rawai to cewa, aikin na daga cikin kasafin kudin shekarar 2021.

Wannan dai na kunshe ne a cikin kasafin kudi na shekarar 2022 na Naira biliyan 278.6 da gwamna Nasir El-Rufai ya sanya wa hannu a ranar Larabar da ta gabata, kuma ya bayyanawa manema labarai a Kaduna ranar Alhamis.

Takardar ta kuma nuna cewa daga cikin Naira biliyan 13.1 da a ka ware wa ma’aikatar ilimi domin gudanar da manyan ayyuka, za a kashe Naira biliyan 1.7 wajen sa baki, domin inganta abinci mai gina jiki a makarantun sakandare na kwana 26 da ke jihar.

Gwamnatin ta kuma ware Naira miliyan 658, domin gyara makarantun sakandire 69 a fadin jihar da kuma Naira miliyan 220, domin samar da kayan daki a makarantun sakandare.

Takardar ta bayyana cewa, za a kashe Naira biliyan 1.49 wajen gyara, kayan aiki da mayar da makarantu 16 a fadin jihar zuwa cikakkun wuraren kwana da kuma Naira miliyan 190.7 wajen sayo kayayyakin kimiyya da fasaha da kuma na sana’o’i.

Sannan ya nuna cewa za a kashe Naira miliyan 500 wajen siyan kayayyakin ilimi da litattafai, yayin da za a kashe Naira miliyan 10.4 wajen kafa da kula da lambunan makarantu a fadin jihar.

Hakazalika, an ware Naira miliyan 500, domin magance bala’o’i da gobara da iska, da ruwan sama a makarantun sakandare 50 da ke fadin jihar.

Gwamnatin jihar ta kuma ware Naira miliyan 20.3, domin gudanar da horon sanin makamar aiki da Jagora da masu ba da shawara a makarantu.

Za a kashe Naira miliyan 150 wajen bunkasa da tura tashar ilimi da kuma wadatar da dandalin ilmantarwa ta shafin internet.

Takardar ta kuma nuna cewa, an ware Naira biliyan 2.2 ga shirin tallafawa ‘yan mata matasa don koyo da karfafawa Bankin Duniya da kuma Naira biliyan 3.0 na hadin gwiwar Global Partnership for Education.

NAN ta rawaito cewa, Naira biliyan 13.1 da a ka ware wa ma’aikatar, domin gudanar da manyan ayyuka ya haura Naira biliyan 10.7 da a ka ware a shekarar 2021.

A cikin kididdigar kasafin kudi na Naira biliyan 278.6, an ware Naira biliyan 94.1 domin kashe kudade na yau da kullum, da kuma Naira biliyan 184.5 na kashe kudade, wanda ya nuna kashi 66.4 na jimillar kasafin kudin.

A cikin kasafin kudin, bangaren ilimi ya samu kaso mafi tsoka na Naira biliyan 69.8, wanda ya nuna kashi 25 cikin 100 da a ka ware biliyan 41.7, domin kashe kudi da kuma Naira biliyan 28 na kashe-kashe akai-akai.

 

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp