Biyu daga cikin wadanda ake zargin sun kashe wata yarinya ‘yar shekara 17 mai suna Sofiat, sun bayyana yadda suka shirya tare da yanke kan yarinyar, domin gamsar da matsalar samun arziki da suka dauka ta hanyar yin al’adar kudi da tsafi.
Wadanda ake zargin, Soliu Majekodunmi mai shekaru 18 da Mustakeem Balogun mai shekaru 19, sun kashe Sofiat ne a ranar Juma’ar da ta gabata a dakin tsohuwar, wadda masoyinta ne, bayan sun yi lalata da ita.
Sauran wadanda ake zargi da aikata laifin sun hada da Gafar Lukmon da Waris Oladeinde.
A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Abimbola Oyeyemi, ya ce, uku daga cikin wadanda ake zargin, Mustakeem, Gafar da Waris an kama su ne da sanyin safiyar ranar Asabar ta hannun ‘yan sanda daga ofishin ‘yan sanda na Adatan, karkashin jagorancin jami’in ‘yan sanda, SP Abiodun Salau, bayan da suka samu rahoto daga shugaban masu gadin al’ummar cewa, an ga wadanda ake zargin suna kona wani abu da ake zargin kan mutum ne a cikin tukunyar yumbu.
Wanda ake zargi na hudu, Soliu, wanda da farko ya tsere bayan ya lura cewa an fallasa su, amma an kama su daga baya.