fidelitybank

Sai da a ka bani guba na sha a Sakatariyar PDP – Wike

Date:

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, a ranar Lahadi, ya bayyana cewa an saka masa guba a sakatariyar jam’iyyar PDP, a shekarar 2018.

Wike ya ce gubar ta shafi hanta da kuma kodarsa, inda ya kara da cewa ta kusa kashe shi amma don Allah.

Ya bayyana hakan ne yayin wani taron godiya na musamman da iyalansa suka shirya a St. Peters Deanery, Rumuepirikom, yankin Obio-Akpor a jihar.

Tsohon gwamnan ya ce an kai shi birnin Beirut ne da tsakar dare, inda likitoci suka sanar da shi cewa hanta da kodarsa sun bace.

A cewar wike, bayan halartar wurinsa, likitoci sun sanar da shi cewa gabobin sun sake aiki.

Ya ce likitocin sun sallame shi bayan kusan mako guda, inda suka bukaci ya dawo gida, tare da bayyana cewa ya sauya tsarin tafiyarsa ne a lokacin yakin neman zabensa karo na biyu.

Tsohon Gwamnan ya ce kowa ya zama wanda ake tuhuma saboda ya yanke shawarar cewa ba zai shiga gidan wani shugaban jam’iyya ba a lokacin yakin neman zabensa.

Da yake ba da labarin yadda ya kusa mutuwa sakamakon guba, Wike ya ce: “Allah ne mai iko, duk wanda ya san yadda muka hau mulki a 2015, ya san akwai tashin hankali.

“Amma Allah ya ganar da mu. Lokacin da kake ofis, mutane da yawa suna tunanin abubuwa suna tafiya daidai da kai. Ba wanda yake son gano matsalolin da kuke fuskanta a matsayin mutum.

“A watan Disambar 2018, ita ce ranar da tsohon shugaban ma’aikata na zai yi godiya. Zan halarci wannan godiyar. Tun daga ranar Lahadi ban taba saukowa daga dakina ba. Ya yi muni.

“Amma wadanda suka halarci liyafar jihar ranar 1 ga watan Janairu na 2019 za su san cewa ban taba yin magana a ranar ba. Sai na zauna na ce wa mataimakin gwamna ya yi magana a madadina. Ina tsammanin an gama.

“Ban san an saka min guba a sakatariyar jam’iyyarmu ba, likitocin bayan an yi musu jinya, sun dawo suka ce min gabobin jikina sun fara aiki.”

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp