Wata gobara mai ƙarfi ta sake tasowa a yankin Los Angeles, wanda ta sa aka fara kwashe dubban mutane daga yankin zuwa wani wurin daban.
Gobarar ta taso ne daga kimanin tafiyar mil 45 wato kilomita 72 ta arewa maso yammacin birnin na Los Angeles a ranar Laraba, a kusa da tafkin Castaic mai tsaunuka da dama, kuma akwai gidajen mutane da makarantu a kusa.
Tuni wutar ta faÉ—aÉ—a zuwa faÉ—in murabba’in Æ™asa 10,000 a ranar Laraba saboda yanayin iska da buji da ake ciki, duk da cewa har yanzu ba ta kai ga cinye wani gida ko wurin kasuwanci ba, sannan mahukunta na cewa sun yi amannar kashe ta kafin ta munana.
Yankin ya sake faÉ—awa cikin shirin kar ta kwana ne saboda ganin yadda waccan wutar dajin ta É—aiÉ—aita jihar.
AÆ™alla mutum 31,000 ne aka ce tilas su bar yankin, sannan an yi wa wasu mutum 23,000 gargaÉ—in cewa akwai buÆ™atar su tashi daga yankin na Los Angeles, ciki har da fursunoni 500 da suma aka kwashe aka sauya musu wuri, kamar yadda wani jami’in tsaron, Robert Luna ya bayyana.
Shugaban hukumar kashe gobara ta Los Angeles, Anthony Marrone ya ce ma’aikatansa suna aiki tuÆ™uru domin shawo kan gobarar, inda ya ce, “mun kashe kusan kashi 15 na wutar zuwa safiyar Alhamis.”
Hukumomi a jihar na cewa wannan wutar ta bambanta da na’ukan wutar dajin da aka fuskanta kwanakin baya, inda aÆ™alla mutum 28 suka rasu, sannan sama da gidaje 10,000 suka lalace.