Asusun kula da ilimin ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce akwai yara dubu 250 da ke fama da matsananciyar yunwa daga cikin yara miliyan 1.2 da aka yi nazari a kansu a jihar Zamfara.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya, NAN, ya rawaito cewa wakiliyar asusun na Unicef, Cristian Munduate ce ta faɗi hakan yayin wani taron manema labarai a birnin Gusau na jihar ta Zamfara ranar Wednesday.
Misis Munduate ta ce a duk yara 10 da ke jihar ɗaya na fuskantar barazanar mutuwa inda kuma yawan yaran da ke fama da matsalar girma ƴan wata ɗaya zuwa shekaru biyar na ƙaruwa inda suka kai kaso 45.2 cikin 1000.