fidelitybank

Rundunar sojin Najeriya ta ƙaryata garkuwa da mutane a kan titin Maiduguri-Damaturu

Date:

 

Rundunar Sojin-ƙasa ta Nijeriya ta ƙaryata raɗe-raɗin da a ke yi cewa an yi garkuwa da matafiya a kan titin Maiduguri-Damaturu ranar 11 ga watan Disamba.
Ado Isa, kakakin rundunar haɗin gwiwa ta 7 ta ‘Operation Haɗin Kai’ a arewa-maso-gabas ya baiyana cewa raɗe-raɗi ne maras tushe.
“Mun samu rahoton raɗe-raɗin da a ke yaɗawa a kafafen sadarwa ranar 11 ga Disamba.
“Haka kuma wasu jaridu ma sun buga jita-jitar cewa wai ISWAP sun yi garkuwa da matafiya a Borgozo a Ƙaramar Hukumar Kaga a Borno.
“To wannan jita-jitar ba ta da tushe kuma ana yaɗa ta ne  domin a kushe ƙoƙarin da “Operation Hadin Kai’ ke yi,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa ƴan Boko Haram ne su ka yi yunƙurin tare hanya a yankin Dole/Bari domin su tada hankalin al’umma.
“Dakarun da ke sintiri da kewaye su ka zo gurin kuma su ka daƙile yunƙurin na su.
“Ba a ɗauke wani matafiyi a ranar Asabar ba, kawai dai aikin ɓatagari da su ke baƙin ciki cewa zan lafiya na dawowa a arewa-maso-gabas,’ in ji Isa, wanda Kanal ne a soja.
Ya kuma jaddada ƙoƙarin da rundunar ke yi na kare  matafiya a titin.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp