fidelitybank

Rundunar Sojin Ƙasa ta yaye sojoji mayaƙa 525

Date:

A yau Litinin ne Rundunar Sojin Ƙasa ta yaye sojoji mayaƙa 525 waɗanda za a kakkai su zuwa bataliyoyi daban-daban a faɗin ƙasar nan.
Da ya ke jawabi a yayin bikin yaye sojojin a sansanin horon sojoji da ke Kachia a Jihar Kaduna, Shugaban Rundunar Sojin Ƙasa na Ƙasa, Laftanal Janar Faruk Yahya ya baiyana cewa Nijeriya ta samu kayan yaƙi domin samun nasarar yaƙi da rashin tsaro.
Ya kuma yi kira ga  dakarun da su jajirce su ga sun kare kayan yaƙin da ga ɓatagari.
Ya ce an tsara horon sojin ne karo na 80 tare da ɗaukar sojoji masu jini a jika domin koya musu ƙwarewa domin a samu rundunoni masu ƙarfi.
Shugaban ya ƙara da cewa horon Ya sakawa sabbin sojin ƙaimi, ƙwarewa da kuma laƙantar yaƙi da a ke buƙata wajen aiwatar da aikin soja daban-daban da a ke bukata wajen kare Nijeriya.
Ya yi kira ga sojin da a ka yaye da su dage su yi amfani da horon da su ka samu a duk inda su ka tsinci kan su a filin daga domin kare ƙasa Nijeriya.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp