fidelitybank

Rundunar ƴan sanda za ta gudanar da taro na kwanaki 3 a kan zaɓen 2023

Date:

Sufeto Janar na ‘yan sanda na ƙasa, Usman Baba ya amince da gudanar da taro na kwanaki uku ga manyan jami’an ‘yan sanda gabanin babban zabe na 2023.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar. Ya ce, taron wani bangare ne na kokarin da rundunar ke yi na tabbatar da zaman lafiya a cikin harkokin tsaron cikin gida da kuma samar da yanayi mai kyau don gudanar da babban zabe a shekarar 2023.

Taron mai taken ‘Muhimmancin tsarin dabarun ‘yan sandan Najeriya don gudanar da zabe cikin lumana’, za a yi shi ne tsakanin ranakun 18 zuwa 21 ga watan Oktoba a Imo.

Sanarwar ta ce, mahalarta taron za su kasance manyan jami’ai masu matsayi na mataimakin sufeto-janar na ‘yan sanda (DIG), mataimakin sufeto-janar na ‘yan sanda (AIG), kwamishinonin ‘yan sanda da sauran shugabannin rundunonin ‘yan sanda.

Ya kara da cewa sauran mahalarta taron za a zabo su a tsanake kan harkokin tsaro da gudanar da zabe a duk fadin duniya, domin su shiga nazari na takwarorinsu da kuma hada ra’ayoyi.

Rundunar ‘yan sandan ta bayyana cewa, za ta tabbatar da gudanar da ingantaccen tsaro kafin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe da kuma ba da dama ga manyan jami’ai su yi mu’amala da manyan jami’an ‘yan uwa na hukumomin tsaro da INEC da kuma abokan huldar ci gaban kasa da kasa.

Ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai shelanta bude taron tare da gabatar da jawabi. Gwamnoni da hafsoshin tsaro da shugabannin sauran hukumomin tsaro da sufeto-janar na ‘yan sanda na baya wasu baki ne da za su halarci taron.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp