fidelitybank

Rufe tashar mu a Zamfara ya sabawa doka – NTA

Date:

Hukumar kula da kafofin yaɗa labarai ta Najeriya ta ce matakin rufe wasu kafofin yaɗa labarai da gwamnatin Jihar Zamfara ta yi ranar Asabar “ya saɓa wa doka”.

Shugaban hukumar ta National Broadcasting Commision (NBC), Balarabe Shehu Ilelah, ya ce sun sanar da gwamnatin Zamfara da ke arewacin ƙasar ƙarara “irin saɓa wa dokar da aka yi”.

“Mun faɗa wa gwamnati ta bai wa al’ummar jihar haƙuri,” a cewarsa cikin wata sanarwa. “Sannan mun shawarci jami’an tsaro da su share umarnin da aka ba su na hana ma’aikatan kafofin da abin ya shafa yin aikinsu na halali.”

A ranar Lahadi Kwamashinan Yaɗa Labarai na Zamfara Ibrahim Dosara ya faɗa wa BBC Hausa cewa an rufe gidajen labaran ne saboda sun yaɗa taron jam’iyyar adawa ta PDP duk da cewa gwamnatin jihar ta hana tarukan siyasa saboda dalilai na tsaro.

Ya ce Majalisar Tsaro ta Zamfara ce ta amince tare da ba da umarnin rufe kafofin labaran da suka ƙunshi Rediyo Najeriya, da Pride FM Gusau, da NTA Gusau, da Gamji Talabijin, da Vision FM, da Al Umma TV.

NBC ta ƙara da cewa “muna kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su guji kawo cikas ga ci gaban da aka samu na dimokuraɗiyya a Najeriya”.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp