Tsohon gwamnan Imo kuma ɗan Majalisar Dattawa, Sanata Rochas Okorocha, ya bayyana sha’awarsa ta tsayawa takarar shugabancin Najeriya a babban zaɓen 2023.
Ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aika wa shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmad Lawan, inda shi kuma ya karanta ta a zaman majalisar na yau Laraba.
Okorocha wanda ɗan jam’iyyar APC ne mai mulkin Najeriya, shi ne tsohon gwamnan Jihar Imo na baya-bayan nan da ke kudu maso gabashin ƙasar.
Shi ne mutum na baya-bayan nan da ya bayyana aniyarsa ta yin takara a APC a zaɓen da za a gudanar tskanin watan Fabarairu zuwa Maris na 2023.
Sauran waɗanda ke fatan su gaji Shugaba Muhammadu Buhari a APC sun haɗa da jagoran jam’iyyar, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Ebonyi David Umahi, da tsohon Gwmnan Abia Sanata Orji Kalu.
Yayin da ake kokarin tunkarar shekarar 2023, wasu daga cikin masu rike da madafun iko a gwamnati da siyasa daban-daban sun fara nuna sha’awarsu na neman ganin jam’iyyun su, sun tsayar da su ‘yan takara a babban zaben 2023.