fidelitybank

Rikicin Siyasa: Zaben wakilai a jam’iyar PDP ya bar baya da kura a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bangar siyasa sun mamaye harabar jam’iyyar PDP a jihar Zamfara, sa’o’i kadan kafin a fara gudanar da zabe wakilai.

Shirin da a ka shirya tun farko na kamfanin man Zaitun dake bayan hukumar alhazai ta jihar, an mayar da shi gidan baki na Command da ke Gusau babban birnin jihar.

A cewar gidan talabijin na Channels, ‘yan barandan sun kai farmaki wurin ne da sanyin safiyar ranar Litinin, inda su ka lalata kayayyakin zabe da fom din tsayawa takara da motoci biyu na ‘yan jam’iyyar tare da kujeru.

Babban Sakataren mataimakin gwamnan Jihar Zamfara, Umar Aminu, ya ce, lamarin ba zai yi wa jam’iyyar barazana ba, ya na mai cewa taron zai gudana kamar yadda a ka tsara.

Ya ce,”Har yanzu ba a san ko su waye ba, kuma na tabbatar da cewa jami’an tsaro za su yi bincike a kai. Ba a dai san ko wace jam’iyya ce ke da alhakin harin da a ka kai a taron jam’iyyar PDP a jihar Arewa maso Yammacin kasar.

Yadda a ka faffasa kujeru tare da kona rumfar zabe a taron PDP

Duk da harin, mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mahdi Gusau da shugaban riko na jam’iyyar Ambasada Bala Mande sun isa sabon wurin taron.

Zaben wakilan kimanin 1,089 wanda za a gudanar da shi da nufin samar da manyan jami’an PDP wadanda za su gudanar da harkokin jam’iyyar.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp