fidelitybank

Rikicin Siyasa: Zaben wakilai a jam’iyar PDP ya bar baya da kura a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bangar siyasa sun mamaye harabar jam’iyyar PDP a jihar Zamfara, sa’o’i kadan kafin a fara gudanar da zabe wakilai.

Shirin da a ka shirya tun farko na kamfanin man Zaitun dake bayan hukumar alhazai ta jihar, an mayar da shi gidan baki na Command da ke Gusau babban birnin jihar.

A cewar gidan talabijin na Channels, ‘yan barandan sun kai farmaki wurin ne da sanyin safiyar ranar Litinin, inda su ka lalata kayayyakin zabe da fom din tsayawa takara da motoci biyu na ‘yan jam’iyyar tare da kujeru.

Babban Sakataren mataimakin gwamnan Jihar Zamfara, Umar Aminu, ya ce, lamarin ba zai yi wa jam’iyyar barazana ba, ya na mai cewa taron zai gudana kamar yadda a ka tsara.

Ya ce,”Har yanzu ba a san ko su waye ba, kuma na tabbatar da cewa jami’an tsaro za su yi bincike a kai. Ba a dai san ko wace jam’iyya ce ke da alhakin harin da a ka kai a taron jam’iyyar PDP a jihar Arewa maso Yammacin kasar.

Yadda a ka faffasa kujeru tare da kona rumfar zabe a taron PDP

Duk da harin, mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mahdi Gusau da shugaban riko na jam’iyyar Ambasada Bala Mande sun isa sabon wurin taron.

Zaben wakilan kimanin 1,089 wanda za a gudanar da shi da nufin samar da manyan jami’an PDP wadanda za su gudanar da harkokin jam’iyyar.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp