Fitaccen malamin addinin musulunci kuma shugaban majalisar malamai ta Kano, Sheikh Ibrahim Khalil ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC.
Da alama dai rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar APC reshen jihar Kano na yin mummunan tasiri a jam’iyyar yayin a cikin ‘yan kwanakin nan tun bayan da a ka fara samun tsagin shugabanci a cikin jam’iyar.
Malam Ibrahim ya bayyana ficewarsa daga cikin jam’iyar APC a cikin zantawarsa da BBC.
Ya ce,“To, a matsayina na dan APC kuma daya daga cikin dattawa kuma daya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar, ina so na tabbatar na fice daga APC,” kamar yadda ya shaida wa BBC.
“Komai na rayuwa ya na da dalili. Dalilai uku ne: ko dai mai ilimi da hankali ya sa ni, ko kuma kowa ya sa ni, ko kuma shi kansa ya san dalili”.
Ya ce ficewar sa daga jam’iyyar ba ta da alaka da zargin da a ke yi masa na tsige shi a matsayin shugaban Majalisar Malamai.
“Idan da haka ne, da na sauka daga mulki. Ba dalili ba ne, domin kamar yadda ban yi bayanin rabuwata da gwamnati ba, ba sai na bata lokaci wajen bayyana ta ba.
“Ban daina siyasa ba kuma ban ce ba zan shiga jam’iyyar ba. Ni da kaina ban shiga ANPP ba, magoya bayana ne su ka yi min rajista. Domin haka yanzu zan shiga jam’iyyar da na ke so da kaina,” inji Malam Ibrahim Khalil.