Kwamitin tsare-tsare na jam’iyyar APC (CECPC) ya nesanta kansa da bangaren Sanata Ibrahim Shekarau na jam’iyyar a jihar Kano.
Shugaban jam’iyyar na kasa, wanda ya bayyana matsayinsa kan taron da aka ce jam’iyar ta gudanar, ta ce ba ta aike da kwamatin zuwa jihar Kano ba.
Sakataren jam’iyyar APC na kasa CECPC, John Akpanudoedehe, wanda ya bayyana hakan a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a Abuja ranar Litinin, ya ce, ba ta da wani kwafin hukuncin da babbar kotun Abuja ta yanke wanda aka ce ta amince da bangaren Shekarau.
PlatinumPost ta rawaito cewa an yi takun-saka tsakanin bangaren Shekarau na APC da bangaren zartaswar APC na jihar Kano, karkashin jagorancin shugabanta, Abdullahi Abbas.
Shugaban jam’iyyar APC da aka sani ya na biyayya ga Gwamna Abdullahi Ganduje.
A wata tattaunawa ta daban, Barista Auwwal Ibrahim wanda ya jagoranci tawagar da ta gudanar da taron majalisar wadda ta samar da Abdullahi Abass a matsayin shugaba, ya shaida wa manema labarai cewa taron da Gwamna Ganduje ya halarta ita ce ta sahihanci.