Jam’iyar APC reshen jihar Kano tsagin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, sun rubuta takardar koke ga sufeto Janar na ‘yan sanda kan ayyukan da tsagin Malam Ibrahim Shekarau ke yi.
A cikin takardar karoafin mai dauke da sa hannun Sanata mai wakiltar mazabar Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya da wasu ‘yan majalisar tarayya da na jihohi 15 da kuma wasu shugabannin kananan hukumomi 15 na jam’iyyar APC, ta bukaci Sufetan ya binciki ‘yan siyasar da abin ya shafa tare da gurfanar da su gaban kuliya idan aka same su da su.
Wadanda aka lissafa a cikin koken sun hada da Sanata Ibrahim Shekarau, Barau Jibrin, Nasiru Abduwa, Tijjani Abdulkadir Jobe, Sha’aban Sharada, Haruna Isa Dederi da kuma Ahmadu Haruna Danzago, wanda a ke yi musu lakabi da G7.
A cikin karar mai dauke da kwanan watan 6 ga watan Disamba, jam’iyyar APC karkashin jagorancin Ganduje ta zargi bangaren Shekarau da laifin haifar da tashin hankali, daukar nauyin tayar da hankulan jama’a, tayar da zaune tsaye, da rashin zaman lafiya, tashin hankalin jama’a da hargitsi a jihar Kano.
Jam’iyyar APC ta Kano ta kuma yi zargin cewa, bangaren Shekarau ya hayo wasu ‘yan baranda da aka yi amfani da su wajen yunkurin kwace sakatariyar jam’iyyar da injina a ranar 30 ga watan Nuwamba bisa zargin cewa wata babbar kotu da ke Abuja ta yanke hukunci a kan su.
Ga hoton kwafin wasikar.