fidelitybank

Rikicin APC: Tsagin Ganduje ya kai karar tsagin Shekarau wajen shugaban ‘yan sanda

Date:

Jam’iyar APC reshen jihar Kano tsagin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, sun rubuta takardar koke ga sufeto Janar na ‘yan sanda kan ayyukan da tsagin Malam Ibrahim Shekarau ke yi.

A cikin takardar karoafin mai dauke da sa hannun Sanata mai wakiltar mazabar Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya da wasu ‘yan majalisar tarayya da na jihohi 15 da kuma wasu shugabannin kananan hukumomi 15 na jam’iyyar APC, ta bukaci Sufetan ya binciki ‘yan siyasar da abin ya shafa tare da gurfanar da su gaban kuliya idan aka same su da su.

Wadanda aka lissafa a cikin koken sun hada da Sanata Ibrahim Shekarau, Barau Jibrin, Nasiru Abduwa, Tijjani Abdulkadir Jobe, Sha’aban Sharada, Haruna Isa Dederi da kuma Ahmadu Haruna Danzago, wanda a ke yi musu lakabi da G7.

A cikin karar mai dauke da kwanan watan 6 ga watan Disamba, jam’iyyar APC karkashin jagorancin Ganduje ta zargi bangaren Shekarau da laifin haifar da tashin hankali, daukar nauyin tayar da hankulan jama’a, tayar da zaune tsaye, da rashin zaman lafiya, tashin hankalin jama’a da hargitsi a jihar Kano.

Jam’iyyar APC ta Kano ta kuma yi zargin cewa, bangaren Shekarau ya hayo wasu ‘yan baranda da aka yi amfani da su wajen yunkurin kwace sakatariyar jam’iyyar da injina a ranar 30 ga watan Nuwamba bisa zargin cewa wata babbar kotu da ke Abuja ta yanke hukunci a kan su.

Ga hoton kwafin wasikar.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp