fidelitybank

Rikicin APC: Tsagin Ganduje ya kai karar tsagin Shekarau wajen shugaban ‘yan sanda

Date:

Jam’iyar APC reshen jihar Kano tsagin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, sun rubuta takardar koke ga sufeto Janar na ‘yan sanda kan ayyukan da tsagin Malam Ibrahim Shekarau ke yi.

A cikin takardar karoafin mai dauke da sa hannun Sanata mai wakiltar mazabar Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya da wasu ‘yan majalisar tarayya da na jihohi 15 da kuma wasu shugabannin kananan hukumomi 15 na jam’iyyar APC, ta bukaci Sufetan ya binciki ‘yan siyasar da abin ya shafa tare da gurfanar da su gaban kuliya idan aka same su da su.

Wadanda aka lissafa a cikin koken sun hada da Sanata Ibrahim Shekarau, Barau Jibrin, Nasiru Abduwa, Tijjani Abdulkadir Jobe, Sha’aban Sharada, Haruna Isa Dederi da kuma Ahmadu Haruna Danzago, wanda a ke yi musu lakabi da G7.

A cikin karar mai dauke da kwanan watan 6 ga watan Disamba, jam’iyyar APC karkashin jagorancin Ganduje ta zargi bangaren Shekarau da laifin haifar da tashin hankali, daukar nauyin tayar da hankulan jama’a, tayar da zaune tsaye, da rashin zaman lafiya, tashin hankalin jama’a da hargitsi a jihar Kano.

Jam’iyyar APC ta Kano ta kuma yi zargin cewa, bangaren Shekarau ya hayo wasu ‘yan baranda da aka yi amfani da su wajen yunkurin kwace sakatariyar jam’iyyar da injina a ranar 30 ga watan Nuwamba bisa zargin cewa wata babbar kotu da ke Abuja ta yanke hukunci a kan su.

Ga hoton kwafin wasikar.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...
X whatsapp