fidelitybank

Rikicin APC: Tsagin Ganduje ya kai karar tsagin Shekarau wajen shugaban ‘yan sanda

Date:

Jam’iyar APC reshen jihar Kano tsagin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, sun rubuta takardar koke ga sufeto Janar na ‘yan sanda kan ayyukan da tsagin Malam Ibrahim Shekarau ke yi.

A cikin takardar karoafin mai dauke da sa hannun Sanata mai wakiltar mazabar Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya da wasu ‘yan majalisar tarayya da na jihohi 15 da kuma wasu shugabannin kananan hukumomi 15 na jam’iyyar APC, ta bukaci Sufetan ya binciki ‘yan siyasar da abin ya shafa tare da gurfanar da su gaban kuliya idan aka same su da su.

Wadanda aka lissafa a cikin koken sun hada da Sanata Ibrahim Shekarau, Barau Jibrin, Nasiru Abduwa, Tijjani Abdulkadir Jobe, Sha’aban Sharada, Haruna Isa Dederi da kuma Ahmadu Haruna Danzago, wanda a ke yi musu lakabi da G7.

A cikin karar mai dauke da kwanan watan 6 ga watan Disamba, jam’iyyar APC karkashin jagorancin Ganduje ta zargi bangaren Shekarau da laifin haifar da tashin hankali, daukar nauyin tayar da hankulan jama’a, tayar da zaune tsaye, da rashin zaman lafiya, tashin hankalin jama’a da hargitsi a jihar Kano.

Jam’iyyar APC ta Kano ta kuma yi zargin cewa, bangaren Shekarau ya hayo wasu ‘yan baranda da aka yi amfani da su wajen yunkurin kwace sakatariyar jam’iyyar da injina a ranar 30 ga watan Nuwamba bisa zargin cewa wata babbar kotu da ke Abuja ta yanke hukunci a kan su.

Ga hoton kwafin wasikar.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...
X whatsapp