fidelitybank

Rikicin APC: Alhakina ne ci gaba da bunkasa Kano da ayyuka – Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya jaddada kudirinsa na ci gaba da bunkasa jihar duk kuwa da yunkurin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo tsaiko a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a gidan gwamnatin jihar Kano, a ranar Lahadin da ta gabata, tare da halartar dukkan bangarorin masu ruwa da tsaki.

Ya ce, “Ya na da matukar muhimmanci kowa ya san cewa hazakarmu ta siyasa da gogewar siyasarmu ba za su bari rikicin kananan jam’iyya ya karkatar da hankalinmu wajen kara bunkasa jiharmu ta Kano ba. Abin da ke faruwa wani bangare ne na al’adar dimokuradiyya,” inji Ganduje yayin da ya ke mayar da martani kan rikicin jam’iyyar APC na Kano.

Sanata Kabiru Ibrahim Gaya da ‘yan majalisar wakilai 20, kakakin majalisar dokokin jihar Kano, da ‘yan majalisar dokokin jihar 28, da shugabannin kananan hukumomi 44, dukkan shugabannin jam’iyyar APC mai mulki daga mazabar 484 da kananan hukumomi 44 da kuma shugabannin jam’iyyar na jihar da dattawan jihar da dai sauran su, wadanda su ka halarci taron, sun kada kuri’ar amincewa da gwamnan.

A cewar sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan jihar, Anwar Abba, wanda PlatinumPost ta samu a ranar Lahadin da ta gabata, Ganduje yayin da ya ke tunatar da masu ruwa da tsaki a kan tsarin da a ka bi a taron gundumomi da na kananan hukumomi na jam’iyyar, ta ce dukkanin hanyoyin sun bi ka’idoji.

A kan shirin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo ruguza sha’anin mulki a jihar, Ganduje ya ce shi ba sabon salo ba ne a irin wannan salon siyasar.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp