fidelitybank

Rikicin APC: Alhakina ne ci gaba da bunkasa Kano da ayyuka – Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya jaddada kudirinsa na ci gaba da bunkasa jihar duk kuwa da yunkurin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo tsaiko a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a gidan gwamnatin jihar Kano, a ranar Lahadin da ta gabata, tare da halartar dukkan bangarorin masu ruwa da tsaki.

Ya ce, “Ya na da matukar muhimmanci kowa ya san cewa hazakarmu ta siyasa da gogewar siyasarmu ba za su bari rikicin kananan jam’iyya ya karkatar da hankalinmu wajen kara bunkasa jiharmu ta Kano ba. Abin da ke faruwa wani bangare ne na al’adar dimokuradiyya,” inji Ganduje yayin da ya ke mayar da martani kan rikicin jam’iyyar APC na Kano.

Sanata Kabiru Ibrahim Gaya da ‘yan majalisar wakilai 20, kakakin majalisar dokokin jihar Kano, da ‘yan majalisar dokokin jihar 28, da shugabannin kananan hukumomi 44, dukkan shugabannin jam’iyyar APC mai mulki daga mazabar 484 da kananan hukumomi 44 da kuma shugabannin jam’iyyar na jihar da dattawan jihar da dai sauran su, wadanda su ka halarci taron, sun kada kuri’ar amincewa da gwamnan.

A cewar sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan jihar, Anwar Abba, wanda PlatinumPost ta samu a ranar Lahadin da ta gabata, Ganduje yayin da ya ke tunatar da masu ruwa da tsaki a kan tsarin da a ka bi a taron gundumomi da na kananan hukumomi na jam’iyyar, ta ce dukkanin hanyoyin sun bi ka’idoji.

A kan shirin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo ruguza sha’anin mulki a jihar, Ganduje ya ce shi ba sabon salo ba ne a irin wannan salon siyasar.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp