Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya kori kwamishinan lafiya na jihar, Farfesa Princewill Chike, sakamakon rashin neman amincewar gwamnatin jihar na karbar bakwancin taron share fage na kungiyar likitoci da hakora ta Najeriya, MDCN, a Fatakwal, babban birnin jihar.
Gwamnan ya bayyana matakin da kwamishinan ya dauka na karbar bakwancin MDCN ba tare da izinin gwamnatin jihar ba a matsayin abin kunya ba.
Gwamna Wike ya sanar da korar Farfesa Chike ne a lokacin da Shugaban MDCN, Farfesa Abba Wasiri Hassan ya kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati da ke Fatakwal a ranar Litinin.
Gwamnan ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ba ta taba neman karbar bakwancin taron share fage na MDCN a Fatakwal ba, ya na mai jaddada cewa, kwamishinan lafiya ya yi kuskuren cewa bai shirya gudanar da taron ba a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke kaddamar da ayyuka.
“A gaskiya ban taɓa ganin abin kunya irin wannan ba a rayuwata. Kowa ya san cewa ba dabi’a ba ce in kawo mutane kuma ba za ku iya halartan su ko bakwanci ba. Domin haka duk wanda ya yi haka zai sha wuya a kansa,” inji shi.
Wike ya kuma ce bukatar da MDCN ta yi na cewa gwamnonin jihohi su samar da manyan asibitoci guda daya a kowace karamar hukumarsu ta majalisar dattawa ba za ta cimma ruwa ba, saboda karancin kudade.
“Kun yi magana a kan samar da babban asibiti a kowace gundumar majalisar dattawa, kun san ba zai yi wu ba. Shi ya sa a Nijeriya muna da matsala. Lokacin da kuka je kasafin ku, kuna sanya kowane nau’in ayyuka. Ka san ba zai iya aiki ba. A ina za ku samu kudin da za a kafa wannan ayyukan a kowace gundumomin”. inji shi.