fidelitybank

Rashin neman amincewar gwamnati: Nyesom Wike ya kori kwamishinan lafiya

Date:

Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya kori kwamishinan lafiya na jihar, Farfesa Princewill Chike, sakamakon rashin neman amincewar gwamnatin jihar na karbar bakwancin taron share fage na kungiyar likitoci da hakora ta Najeriya, MDCN, a Fatakwal, babban birnin jihar.

Gwamnan ya bayyana matakin da kwamishinan ya dauka na karbar bakwancin MDCN ba tare da izinin gwamnatin jihar ba a matsayin abin kunya ba.

Gwamna Wike ya sanar da korar Farfesa Chike ne a lokacin da Shugaban MDCN, Farfesa Abba Wasiri Hassan ya kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati da ke Fatakwal a ranar Litinin.

Gwamnan ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ba ta taba neman karbar bakwancin taron share fage na MDCN a Fatakwal ba, ya na mai jaddada cewa, kwamishinan lafiya ya yi kuskuren cewa bai shirya gudanar da taron ba a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke kaddamar da ayyuka.

“A gaskiya ban taɓa ganin abin kunya irin wannan ba a rayuwata. Kowa ya san cewa ba dabi’a ba ce in kawo mutane kuma ba za ku iya halartan su ko bakwanci ba. Domin haka duk wanda ya yi haka zai sha wuya a kansa,” inji shi.

Wike ya kuma ce bukatar da MDCN ta yi na cewa gwamnonin jihohi su samar da manyan asibitoci guda daya a kowace karamar hukumarsu ta majalisar dattawa ba za ta cimma ruwa ba, saboda karancin kudade.

“Kun yi magana a kan samar da babban asibiti a kowace gundumar majalisar dattawa, kun san ba zai yi wu ba. Shi ya sa a Nijeriya muna da matsala. Lokacin da kuka je kasafin ku, kuna sanya kowane nau’in ayyuka. Ka san ba zai iya aiki ba. A ina za ku samu kudin da za a kafa wannan ayyukan a kowace gundumomin”. inji shi.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp