fidelitybank

Rashin neman amincewar gwamnati: Nyesom Wike ya kori kwamishinan lafiya

Date:

Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya kori kwamishinan lafiya na jihar, Farfesa Princewill Chike, sakamakon rashin neman amincewar gwamnatin jihar na karbar bakwancin taron share fage na kungiyar likitoci da hakora ta Najeriya, MDCN, a Fatakwal, babban birnin jihar.

Gwamnan ya bayyana matakin da kwamishinan ya dauka na karbar bakwancin MDCN ba tare da izinin gwamnatin jihar ba a matsayin abin kunya ba.

Gwamna Wike ya sanar da korar Farfesa Chike ne a lokacin da Shugaban MDCN, Farfesa Abba Wasiri Hassan ya kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati da ke Fatakwal a ranar Litinin.

Gwamnan ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ba ta taba neman karbar bakwancin taron share fage na MDCN a Fatakwal ba, ya na mai jaddada cewa, kwamishinan lafiya ya yi kuskuren cewa bai shirya gudanar da taron ba a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke kaddamar da ayyuka.

“A gaskiya ban taɓa ganin abin kunya irin wannan ba a rayuwata. Kowa ya san cewa ba dabi’a ba ce in kawo mutane kuma ba za ku iya halartan su ko bakwanci ba. Domin haka duk wanda ya yi haka zai sha wuya a kansa,” inji shi.

Wike ya kuma ce bukatar da MDCN ta yi na cewa gwamnonin jihohi su samar da manyan asibitoci guda daya a kowace karamar hukumarsu ta majalisar dattawa ba za ta cimma ruwa ba, saboda karancin kudade.

“Kun yi magana a kan samar da babban asibiti a kowace gundumar majalisar dattawa, kun san ba zai yi wu ba. Shi ya sa a Nijeriya muna da matsala. Lokacin da kuka je kasafin ku, kuna sanya kowane nau’in ayyuka. Ka san ba zai iya aiki ba. A ina za ku samu kudin da za a kafa wannan ayyukan a kowace gundumomin”. inji shi.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...
X whatsapp