Shugaban kasar Malawi, Lazarus Chakwera, ya kori dukannin ministocinsa, bisa zargin cin hanci da rashawa.
A wani jawabi da ya yi ga al’ummar kasar ta talabijin a ranar Litinin, shugaban ya lashi takobin tunkarar duk wata matsalar kin bin doka daga jami’an gwamnati.
Ya ce, za a kafa wata sabuwar majalisar ministocin cikin kwana biyu.
Ministoci uku na fuskantar tuhuma, wadanda suka hada da ministan kula da harkokin filaye, wanda aka kama a watan da ya gabata a kan zargin cin hanci.
Shi kuwa ministan kwadago ana zarginsa ne da karkatar da kudin yaki da annobar korona, yayin da ministan makamashi ke fuskantar zargin almundahana a kwangilolin mai.
Shugaban Malawai, Lazarus, ya na zargin kafatanin ministocin sa, wanda suka musanta zargin.
An zabi Mista Chakwera a shekarar 2020, inda ya yi alkawarin yakar cin hanci da rashawa.
A makon da ya wuce wasu kungiyoyin coci biyu masu karfin fadi a ji suka zargi shugaban da cewa ba ya kokari wajen yaki da matsalar cin hanci.