Kasar Rasha ta aike da dakarun sojojin ta zuwa kasar Kazakhstan, domin taimakawa wajen kawo karshen tarzomar da ta barke a fadin kasar, bayan munanan tashe-tashen hankula da suka bazu a cikin tsohuwar gwamnatin Tarayyar Soviet.
‘Yan sanda sun ce sun kashe masu zanga-zanga da dama a babban birnin Almaty na tsakiyar yankin Asiya. Gidan talabijin din kasar ya ce, jami’an tsaro 13 ne suka mutu, ciki har da biyu da aka samu an yanke kawunansu.
Kamfanin dillancin labarai na Rueters ya rawaito cewa, wani gidan shugaban kasa da ofishin magajin gari da ke birnin, duk sun kone kurmus, sai dai ya zuwa yammacin ranar Alhamis, filin jirgin saman birnin, wanda masu zanga-zangar suka kwace tun da farko, ya na karkashin kulawar jami’an soji, yayin da motocin da suka kone sun cika titunan kasar.
Da sanyin safiyar Alhamis din nan, wasu dakaru masu sulke da dakaru da dama ne suka shiga babban birnin na Almaty, kuma a na jin karar harbe-harbe a lokacin da sojoji su ka tunkari taron, kamar yadda wakilan kamfanin dillancin labaran Reuters suka rawaito daga wurin.