fidelitybank

Rasha ta aike da dakarun soji zuwa Kazakhstan

Date:

Kasar Rasha ta aike da dakarun sojojin ta zuwa kasar Kazakhstan, domin taimakawa wajen kawo karshen tarzomar da ta barke a fadin kasar, bayan munanan tashe-tashen hankula da suka bazu a cikin tsohuwar gwamnatin Tarayyar Soviet.

‘Yan sanda sun ce sun kashe masu zanga-zanga da dama a babban birnin Almaty na tsakiyar yankin Asiya. Gidan talabijin din kasar ya ce, jami’an tsaro 13 ne suka mutu, ciki har da biyu da aka samu an yanke kawunansu.

Kamfanin dillancin labarai na Rueters ya rawaito cewa, wani gidan shugaban kasa da ofishin magajin gari da ke birnin, duk sun kone kurmus, sai dai ya zuwa yammacin ranar Alhamis, filin jirgin saman birnin, wanda masu zanga-zangar suka kwace tun da farko, ya na karkashin kulawar jami’an soji, yayin da motocin da suka kone sun cika titunan kasar.

Da sanyin safiyar Alhamis din nan, wasu dakaru masu sulke da dakaru da dama ne suka shiga babban birnin na Almaty, kuma a na jin karar harbe-harbe a lokacin da sojoji su ka tunkari taron, kamar yadda wakilan kamfanin dillancin labaran Reuters suka rawaito daga wurin.

 

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp