Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya yabawa mahaifiyarsa, marigayiya Hajiya A’isha Kande da ta raine shi, shi kadai a lokacin da mahaifinsa ya rasu.
Atiku Abubakar, a wani rubutu da ya rubuta a yau, 7 ga watan Maris, domin tunawa da ranarĀ mata ta duniya da za ta zo gobe 8 ga watan Maris, ya ce, a yau, akwai Aisha Kande da dama, wadda a kullum tarihinta na wahala da wahala wajen tarbiyar āyaāya masu kwazo.
Atiku ya ce, āIna binta da yawa daga abin da na zama a rayuwa ga Allah da kuma ga mahaifiyata marigayiya, Hajiya Aisha Kande. Na rasa mahaifina tun ina karami. Domin haka, a zahiri, ni samfurin haihuwa ce ta mahaifiyata.ā
āDukkanin su a matsayin masu taimaka wa mazajensu ko matan da mazansu suka mutu kamar marigayiya mahaifiyata, matan da suka yi nasara da suka jure duk wata matsala wajen tarbiyyantar da āyaāyansu da tarbiyya da ilimi su ne ainihin jaruman da muke bikin a yau.