A ci gaba da gasar Firimiyar kasar Ingila, kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta kwaci maki guda a hannun Chelsea a filin wasa na Stamford Bridge.
Wasan mako na 13 da aka fafata a yammacin ranar Lahadi, dan wasan gaba na Manchester United Jardon Sancho ne ya zura kwallon farko a minti 50, yayin da dan wasan Chelsea Jorginho ya farke kwallo a minti 69 a bugun daga kai sai mai tsaron raga.
Yanzu haka Chelsea na da maki 30, Manchester City na da maki 29 sai Liverpool ta na da maki 28.