fidelitybank

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Date:

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar Labour, Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu.

Yunusa ya bayyana haka ne a wajen taron ƙungiyar da aka yi a jihar Oyo, wanda aka tara ƴan siyasa da masana da ƙungiyoyin siyasa a jihar domin tattaunawa game da siyasar ƙasar.

Jaridar Daily Trust ce ta ruwaito shugaban ƙungiyar yana bayyana hakan, inda ya ce, “domin warware shubuha da ake ciki, har yanzu Peter Obi ɗan Jam’iyyar Labour ne. Kun dai san akwai wasu matsaloli a jam’iyyar waɗanda ake jiran INEC ta kawo maslaha a game da su.”

Ya ƙara da cewa idan aka zaɓi Obi a matsayin shugaban Najeriya, “wa’aɗi ɗaya zai yi, kuma a wannan wa’adin ɗayan ne zai kawo canjin da ake buƙata. Yawancin matsalolin da muke fuskanta za a iya magance su a shekara ɗaya idan aka yi abun da ya dace. Kuma zai iya domin ya yi an gani a lokacin da yake gwamnan jihar Anambra.”

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam...

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...
X whatsapp