fidelitybank

PDP na jiran hukuncin kotu a kan ‘yan takarar gwamnan Taraba

Date:

Hankali ya tashi a jihar Taraba yayin da mambobin jam’iyyar PDP, ke jiran hukuncin kotun koli kan dan takarar gwamnan jam’iyyar.

DAILY POST ta samu cewa za a yanke hukuncin ne a yau Juma’a.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kadan bayan da kotun ta soke zaben fidda gwani na takarar gwamna da jam’iyyar APC ta gudanar.

Daya daga cikin ‘yan takarar gwamna a jam’iyyar PDP, Farfesa Jerome Nyameh ya garzaya kotun koli bayan da kotun daukaka kara ta yi watsi da karar da ya shigar a kan dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP Kefas Agbu, bisa hujjar cewa shi (Agbu) bai sayi fom din nuna sha’awa da tsayawa takara ba.

Karanta Wannan: Zan ruguza PDP da ‘yan cikinta – Dan PDP a jawabin taron nnpp

Ya bayar da hujjar ta bakin lauyansa, Pius D. Pius cewa dan takarar shi ne shugaban jam’iyyar na jihar, wanda ya ce shi ne ya jagoranci tantance wasu masu neman tsayawa takarar mukamai daban-daban a dandalin jam’iyyar.

A lokacin shigar da wannan rahoto, tashin hankali ya mamaye sansanonin Agbu da Nyameh.

Wasu daga cikin magoya bayan nasu da suka zanta da DAILY POST, sun ce za su amince da sakamakon hukuncin da za a yanke cikin gaskiya.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp