Jam’iyyar PDP ta ce ba ta sanya tikitin takarar shugaban kasa a 2023 ba.
Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ne ya bayyana hakan yayin da a ke yaɗa jita-jitar.
Ya ce, “Hankalin jam’iyyar PDP ya dawo kan ta, sakamakon ce-ce-ku-cen da wasu mutane da ke ikirarin cewa jam’iyyar mu ta sanya tikitin tsayawa takarar shugaban kasa a wani yanki na kasar nan.
“Wannan kwata-kwata yaudara ce, domin ba ya wakiltar matsayin jam’iyyarmu ta kowace hanya, domin haka ku yi watsi da wannan raɗe-raɗin.
“Domin kaucewa shakku, PDP ta fito karara ba tare da wata shakka ba, ta ce ba ta sanya mata tikitin tsayawa takarar shugaban kasa a wani bangare na kasar nan ba”. In ji Debo.