Bulaliyar majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya ziyarci shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) da ake tsare da shi a ofishin DSS dake Abuja.
Tsohon gwamnan jihar Abia, wanda ya bayyana hakan a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Litinin, ya ce yana da cikakkiyar masaniyar cewa Kanu ya na tattara mabiya ta hanyar neman ‘yancinsa.
Kalamansa: “Da yammacin yau, na ziyarci dan uwana, Maazi Nnamdi Kanu a hannun DSS, Abuja. Na same shi cikin koshin lafiya da kulawa kuma muka tattauna a matsayin ‘Umunne’. A 2001 lokacin da na ke Gwamna na ziyarci mahaifinsa Eze Israel Okwu Kanu sarkin gargajiya na Akwara Ukwu, kuma tun a lokacin dangi sun kasance kusa da ni sosai. Na fahimci cewa Nnamdi ya na da mahaukatan mutane da suka kafe shi a bayansa kuma na Æ™arfafa shi ya yi la’akari da illar wasu ayyuka da maganganu, domin kare kansu. Ko da ya ke, akida na da akidarsa sun bambanta, Allah ya sa mu zama ‘yan’uwa kuma ba za mu iya guje wa juna ba. Ina bashi shawara da yan Najeriya nasiha mai kyau…Ko shi da iyalinsa sun saurare ni ko ba su saurare ni ba, zan ci gaba da yi masa nasiha kamar yadda na saba yi a baya. Abin da muke bukata shi ne zaman lafiya da kwanciyar hankali.”