fidelitybank

Orji Kalu ya bayyana burin sa na takarar shugaban kasa

Date:

Tsohon gwamnan jihar Abia, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana burinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

A zantawarsa da manema labarai ranar Talata a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja, Kalu ya kuma yabawa kungiyoyin da su ka amince da shi ta hanyar lika hotunan yakin neman zabensa a fadin kasar.

Kalu ya ce, ya na shirin yin takara a matsayi na daya a kasar nan, idan jam’iyyar APC mai mulki ta tsayar da tikitin takarar shugaban kasa a yankin Kudu maso Gabas.

Tsohon gwamnan ya bayyana kwarin gwiwar cewa, jam’iyya mai mulki za ta samar da shugaban da zai yi aiki da hadin kan kasa.

Sai dai Kalu ya yabawa kungiyoyin da su ka tuntube shi, domin ya tsaya takarar shugaban kasa, kuma su ka same shi da ya cancanta ya samar da kyakkyawan shugabanci ga al’umma.

Ya ce: “Ina so in ci gaba da gode wa mutanen da su ke sanya hoto na a duk fadin Najeriya, ban yanke shawarar tsayawa takarar shugaban kasa ba ko a’a.

“Amma idan an baiwa yankin Kudu maso Gabas dama, zan sake tunani in ga ko akwai hakan, domin jam’iyyar ba ta bayyana inda suka ware shugaban kasa ba.

“Amma na san jam’iyyar za ta kawo shugaban da zai yi aikin hadin kan kasa wanda ya fi muhimmanci.” A cewar Orji.

Sai dai Kalu, wanda ke komawa Abuja bayan hutun Kirsimeti da na sabuwar shekara, ya bayyana cewa, ya na tuntubar masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa kan kudirinsa na tsayawa takarar shugabancin kasar.

Kalaman Kalu sun biyo bayan sanarwar da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Asiwaju Bola Tinubu ya yi na zama shugaban kasa a 2023.

Tsohon gwamnan jihar Legas ya tabbatar da cewa ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

Da ya ke magana da manema labarai a fadar gwamnatin a ranar Litinin, Tinubu ya ce, bai sanar da ‘yan Najeriya burinsa ba, saboda har yanzu ya na tuntubar masu ruwa da tsaki.

 

 

 

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp