fidelitybank

Orji Kalu ya bayyana burin sa na takarar shugaban kasa

Date:

Tsohon gwamnan jihar Abia, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana burinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

A zantawarsa da manema labarai ranar Talata a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja, Kalu ya kuma yabawa kungiyoyin da su ka amince da shi ta hanyar lika hotunan yakin neman zabensa a fadin kasar.

Kalu ya ce, ya na shirin yin takara a matsayi na daya a kasar nan, idan jam’iyyar APC mai mulki ta tsayar da tikitin takarar shugaban kasa a yankin Kudu maso Gabas.

Tsohon gwamnan ya bayyana kwarin gwiwar cewa, jam’iyya mai mulki za ta samar da shugaban da zai yi aiki da hadin kan kasa.

Sai dai Kalu ya yabawa kungiyoyin da su ka tuntube shi, domin ya tsaya takarar shugaban kasa, kuma su ka same shi da ya cancanta ya samar da kyakkyawan shugabanci ga al’umma.

Ya ce: “Ina so in ci gaba da gode wa mutanen da su ke sanya hoto na a duk fadin Najeriya, ban yanke shawarar tsayawa takarar shugaban kasa ba ko a’a.

“Amma idan an baiwa yankin Kudu maso Gabas dama, zan sake tunani in ga ko akwai hakan, domin jam’iyyar ba ta bayyana inda suka ware shugaban kasa ba.

“Amma na san jam’iyyar za ta kawo shugaban da zai yi aikin hadin kan kasa wanda ya fi muhimmanci.” A cewar Orji.

Sai dai Kalu, wanda ke komawa Abuja bayan hutun Kirsimeti da na sabuwar shekara, ya bayyana cewa, ya na tuntubar masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa kan kudirinsa na tsayawa takarar shugabancin kasar.

Kalaman Kalu sun biyo bayan sanarwar da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Asiwaju Bola Tinubu ya yi na zama shugaban kasa a 2023.

Tsohon gwamnan jihar Legas ya tabbatar da cewa ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

Da ya ke magana da manema labarai a fadar gwamnatin a ranar Litinin, Tinubu ya ce, bai sanar da ‘yan Najeriya burinsa ba, saboda har yanzu ya na tuntubar masu ruwa da tsaki.

 

 

 

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp