fidelitybank

Orji Kalu ya raba tallafin Babura da abinci da kudade a yankin sa

Date:

Bulaliyar majalisar dattijawa, Orji Uzor Kalu, ya bayar da tallafin Babura da kayan abinci tare da kyautar kudi ga al’ummar yankuna 13 na Igbere.

Tallafin dai wani yunkuri ne na ƙara ƙarin kayan aikin samar da tsaro a ƙauyena na Igbere.

Rabon tallafin kayayyakin wanda ya gudana a yammacin ranar Talata wanda Bulaliyar majalisar dattiawa mai wakiltar Abia ta Arewa a Majalisar ta Tara, Sanata Orji Uzor Kalu ya ba da gudummawar Babura da kayan abinci da tsabar kuɗi ga al’ummomi 13 da su ka haɗa da Igbere.

An mika wadannan kayayyaki kai tsaye ga ‘yan banga a kauyen a gaban shugaban kungiyar jin dadin jama’a na Igbere, Comrade Goddswill .A. Okorie.

Babura da kayan abincin da Kalu ya rabawa al’ummar sa.

Idan kuma za a iya tunawa, Bualiliyar majalisar dattawa, ya duba ayyukan gina tituna sama da 50 a yankin Abia ta Arewa, kafin ya nufi Ezumezu, wajen wani kayan adana kayan tarihi na gargajiya da a ke gudanarwa duk watan Disamba a Igbere na jihar Abia.

Sanata ya kasance abin koyi na ci gaban al’umma. Ya wakilci mazabar Abia ta Arewa da kyau a Majalisar Dokoki ta kasa, a tarihin shekaru biyu da rabin da ya kwashe a zauren majalisar.

Kalu tare da mutanen da su ka samu tagomashin sa.

Mazabar Abia ta Arewa na matukar godiya da irin tasirin da ya ke da shi a fannin tattalin arziki, hadin kai da ci gaban ababen more rayuwa a fadin Abia ta Arewa.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp