Hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya (NCDC) ta ce ta samu ƙarin mutum uku da ke ɗauke da sabon nau’in korona na Omicron a ƙasar.
Wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Talata ta ce, yanzu haka jumillar mutum Shida ne ke ɗauke da Omicron a Najeriya.
Ta ƙara da cewa dukkan mutanen da suka harbu da cutar sun yi balaguro zuwa Afirka ta Kudu a ‘yan kwanakin nan.
Tuni ƙasashen Birtaniya da Kanada suka hana matafiya daga Najeriya shiga ƙasashensu saboda sabon nau’in cutar, matakin da ‘yan Najeriyar suka bayyana a matsayin wariya.
Tun a ranar 1 ga watan Disamba ne dai hukumar ta bayar da rahoton mutum uku na farko da ta tabbatar sun kamu da cutar.