Shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu ya sake shigar da sabuwar kara ga babban Lauyan gwamnatin tarayya (AGF) da ministan shari’a Abubakar Malami (SAN) da kuma hukumar tsaro ta farin kaya (DSS).
A halin yanzu dai shugaban mai fafutukar kafa kasar Biafra ya na fuskantar shari’a kan ta’addanci da kuma cin amanar kasa.
A karar da ya shigar a ranar Litinin, Kanu na neman umarnin babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tilastawa ‘yan sandan sirrin Najeriya, DSS da su ba shi damar samun abinci, kula da lafiya da canza tufafi kamar yadda mai shari’a Binta Nyako ta bayar a baya.
Lauyan sa Barista Maxwell Chibuike Okpara ne ya shigar da karar mai lamba FHC/ABJ/CS1585/2021 a madadin shugaban kungiyar ta IPOB.
Kanu ya kuma nemi a ba shi umarnin tilastawa hukumar DSS ta ba shi damar shirya abincinsa, wanda a shirye ya ke ya biya.
Har ya zuwa yanzu dai, ba a sanya ranar da za a saurari karar ba.
Mai shari’a Nyako a ranar 2 ga watan Disamba ya umarci hukumar DSS da ta baiwa Kanu damar gudanar da addininsa cikin walwala da jin dadin zaman gidan ajiya da gyaran hali.