fidelitybank

Nnamdi Kanu ya sake shigar da kara a kan cimmaka da lafiyar sa

Date:

Shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu ya sake shigar da sabuwar kara ga babban Lauyan gwamnatin tarayya (AGF) da ministan shari’a Abubakar Malami (SAN) da kuma hukumar tsaro ta farin kaya (DSS).

A halin yanzu dai shugaban mai fafutukar kafa kasar Biafra ya na fuskantar shari’a kan ta’addanci da kuma cin amanar kasa.

A karar da ya shigar a ranar Litinin, Kanu na neman umarnin babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tilastawa ‘yan sandan sirrin Najeriya, DSS da su ba shi damar samun abinci, kula da lafiya da canza tufafi kamar yadda mai shari’a Binta Nyako ta bayar a baya.

Lauyan sa Barista Maxwell Chibuike Okpara ne ya shigar da karar mai lamba FHC/ABJ/CS1585/2021 a madadin shugaban kungiyar ta IPOB.

Kanu ya kuma nemi a ba shi umarnin tilastawa hukumar DSS ta ba shi damar shirya abincinsa, wanda a shirye ya ke ya biya.

Har ya zuwa yanzu dai, ba a sanya ranar da za a saurari karar ba.

Mai shari’a Nyako a ranar 2 ga watan Disamba ya umarci hukumar DSS da ta baiwa Kanu damar gudanar da addininsa cikin walwala da jin dadin zaman gidan ajiya da gyaran hali.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...
X whatsapp