fidelitybank

Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun kafa ƙungiya

Date:

Ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso sun ƙaddamar da sabuwar ƙungiyar ƙawancen sojin ƙasashen yankin Sahel.

Ƙasashen sun amince da kafa ƙungiyar ‘Alliance of States of the Sahel’ (AES) wato ‘Ƙawancen ƙasashen yankin Sahel’, bayan wani taro da suka gudanar a birnin Bamako na ƙasar Mali. In ji BBC.

Taron – wanda ya samu halartar shugaban gwamnatin mulkin sojin Mali Kanal Assimi Goita, da ministocin ƙasashen wajen Mali da Burkina Faso da mai magana da yawun gwamnatin mulkin sojin Nijar – ya amince da kafa ƙungiyar don kare ƙasashen yankin Sahel.

Manufar kafa ƙungiyar ita ce samar da tsaron ‘haɗin gwiwwa’ tsakanin ƙasashen uku, ta hanyar yin aiki tare domin yaƙar ‘ta’addanci’ da ‘yan tawaye a cikin ƙasashen uku.

Haka kuma ƙungiyar ta amince da kai wa juna agaji idan ta samu farmaki daga waje.

“Duk wani hari da aka kai wa ɗaya daga cikin ƙasashen ƙungiyar , AES za ta ɗake shi ne tamkar hari a kan duka mambobinta, don haka za ta ɗauki matakin ramuwar gayya, a ƙungiyance ko daban-daban, ciki har da amfani da ƙarfin soji domin tabbatar da zaman lafiya a ƙasashe mambobin ƙungiyar,” kamar yadda yarjejeniyar ta nuna.

Ana kallon kafa wannan ƙawance tamkar martanin ƙasashen uku ne, kan barazanar da Ecowas ke yi na amfani da ƙarfin soji, don mayar da Nijar kan tafarkin dimokraɗiyya bayan da sojojin ƙasar suka kifar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Mohamed bazoum cikin watan Yuli.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp