Kasurgumin dan ta’addar nan da ya addabi wasu yankunan jihohin, Zamfara da Sokoto da kuma Katsina, Bello Turji, ya nemi ya ajiye makamansa, domin a tsagaita zubar da jini daga dukkan bangarorin biyu.
A cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan 14 ga watan Disamban 2021, Turji ya bukaci shugaban kasa, Muhammadu Buhari da Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle da kuma Sarkin Shinkafi, kan bukatar tasa.
Wani mazaunin garin Shinkafi, wanda mamba ne a kwamitin zaman lafiya na garin, ya tabbatar wa da Aminiya sahihancin wasikar mai shafi uku a ranar Lahadi.
Wannan dai ba shi ne karo na farko ba da dan ta’addar ke aike wa yankunan wasika ba. Ko a watan Satumban da ya gabata, ya rubuta wata wasika da shi da wani dan ta’addar, Halilu Sububu, su na gargadin mutane cewa za su kai musu hare-hare.
Neman sulhun nasa dai na zuwa ne a daidai lokacin da jami’an tsaron Najeriya suka zafafa kai hare-hare ga ’yan ta’addar ta sama da kuma ta kasa.