Akalla mutane 15 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka jikkata a wani hari da a ka kai a wani masallaci a kauyen Ba’are da ke karamar hukumar Mashegu a jihar Neja.
Rahotanni sun ce maharan sun kai harin ne a lokacin da mutanen kauyen ke gudanar da sallar Asuba.
Wata majiya ta ce an kai wadanda suka samu raunuka zuwa babban asibitin Kontagora domin yi musu magani.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja, Monday Bala Kuryas, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce akalla mutane 9 ne suka mutu a harin.
“Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta riga ta tura jami’an tsaro zuwa yankin da abin ya shafa, domin kara kare rayuka da dukiyoyin al’umma,” inji Monday.