fidelitybank

NDLEA ta kama ƙwayoyi mai nauyin tan 2.1 a Kano

Date:

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kama wasu mutane 352 da ake zargi tare da kama tan 2.1 na haramtattun kwayoyi a jihar Kano.

Kwamandan NDLEA a jihar, Abubakar Idris-Ahmad, ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na (NAN) a Kano ranar Alhamis.

Idris-Ahmad ya ce, an kama mutanen ne a tsakanin watan Janairu zuwa Maris.

Ya ce wadanda ake zargin sun hada da maza 208 da mata 44, yayin da magungunan da aka kama sun hada da kilogiram 955.304 na tabar wiwi, da Codeine da Tramadol kilogiram 1,225.05.

Sauran a cewarsa, sun hada da gram 25 na hodar iblis, gram 17 na tabar heroin da gram 52 na methamphetamine.

Kwamandan ya ce babban kalubalen da ke gaban hukumar a jihar shi ne shawo kan al’umma wajen bankado masu safarar miyagun kwayoyi a tsakaninsu.

“Kalubalen mu shine samun damar ilimantar da al’umma don samar da bayanai masu amfani game da maboyar masu amfani da muggan kwayoyi ko dillalan da ayyukansu suka ci gaba da yin illa ga al’umma.

“Ya kamata jama’a su lura da illolin da masu shan muggan kwayoyi ko masu safarar miyagun kwayoyi ke haifarwa a cikin al’umma ta yadda jama’a za su fito da bayanai masu amfani don tabbatar da al’ummar da ba ta da miyagun kwayoyi,” inji Idris-Ahmad.

Don haka ya yi kira ga jama’a da su rika bayar da bayanai masu amfani kuma a kan lokaci kan masu safarar miyagun kwayoyi ga rundunar, ta yadda za a fitar da su daga yawo da kuma kare al’umma.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp