fidelitybank

NDLEA ta kama ƙwayoyi mai nauyin tan 2.1 a Kano

Date:

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kama wasu mutane 352 da ake zargi tare da kama tan 2.1 na haramtattun kwayoyi a jihar Kano.

Kwamandan NDLEA a jihar, Abubakar Idris-Ahmad, ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na (NAN) a Kano ranar Alhamis.

Idris-Ahmad ya ce, an kama mutanen ne a tsakanin watan Janairu zuwa Maris.

Ya ce wadanda ake zargin sun hada da maza 208 da mata 44, yayin da magungunan da aka kama sun hada da kilogiram 955.304 na tabar wiwi, da Codeine da Tramadol kilogiram 1,225.05.

Sauran a cewarsa, sun hada da gram 25 na hodar iblis, gram 17 na tabar heroin da gram 52 na methamphetamine.

Kwamandan ya ce babban kalubalen da ke gaban hukumar a jihar shi ne shawo kan al’umma wajen bankado masu safarar miyagun kwayoyi a tsakaninsu.

“Kalubalen mu shine samun damar ilimantar da al’umma don samar da bayanai masu amfani game da maboyar masu amfani da muggan kwayoyi ko dillalan da ayyukansu suka ci gaba da yin illa ga al’umma.

“Ya kamata jama’a su lura da illolin da masu shan muggan kwayoyi ko masu safarar miyagun kwayoyi ke haifarwa a cikin al’umma ta yadda jama’a za su fito da bayanai masu amfani don tabbatar da al’ummar da ba ta da miyagun kwayoyi,” inji Idris-Ahmad.

Don haka ya yi kira ga jama’a da su rika bayar da bayanai masu amfani kuma a kan lokaci kan masu safarar miyagun kwayoyi ga rundunar, ta yadda za a fitar da su daga yawo da kuma kare al’umma.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...

Na ki marawa Atiku baya ne saboda juyin yankin Kudu ne – Wike

Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, a wata...

An saki sakamakon jarabawar WASSCE

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma ta fitar da...

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa wajen karbar abinci

Rahotanni daga Gaza na cewa sojojin Isra'ila sun sake...

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da...

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwandon Afrika

Tawagar ƴan wasan kwando na matan Najeriya ta lashe...

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce ɗaya...

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...
X whatsapp